Malaman Kaduna da Elrufai sun shata layi
Malaman makaranta a jihar Kaduna sun shiga wani yajin aikin "sai baba ta gani" domin nuna fushinsu kan korar malaman da ba su ci jarrabawa ba da gwamnati ta yi. To amma gwamnatin jihar ta ce za ta kori duk malamin da ya shiga yajin aikin.